Gwamnatin Mulkin Sojin Nijar ta Bayar da Umurnin Fitar da Jakadan Faransa da ke ƙasar

 

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta bayar da umurnin fitar da jakadan Faransa da ke ƙasar, inda ta ce a yanzu ya rasa kariyarsa ta diflomasiyya.

Mista Sylvain Itte ya ci gaba da zama a Nijar duk da cikar wa’adin sa’o’i 48 da aka ba shi na ya fice daga cikin ƙasar a ranar Juma’ar da ta gabata.

Sai dai gwamnatin Faransa ta bayyana cewa jakadanta a Nijar bai zai fice daga ƙasar ba saboda gwamnatin sojojin ba ta da hallaci.

Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Faransa ta fitar ta ce “muna nazari a tsaron lafiya da kuma kariya a ofishin jakadancinmu.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com