Sauya Naira: APC ta Goyi Bayan Gwamnoni, ta Bukaci Buhari ya Mutunta Doka

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta sake kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya tsoma baki cikin manufofin tsuke bakin aljihu da ke kawo wa mutane wahala.

Shugaban jam’iyyar, Sanata Abdullahi Adamu, a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan kusan sa’o’i 2 na ganawar sirri da gwamnonin APC, ya ce jam’iyyar za ta tabbatar da hukuncin da kotun koli ta yanke wanda ke rike da ka’idar doka ta tsofaffin takardun kudi.

Adamu ya ce, ya kamata babban bankin Najeriya (CBN) da babban lauyan gwamnatin tarayya (AGF) su mutunta doka ta hanyar tabbatar da hukuncin da kotun koli ta yanke kan musayar kudade.

Ya ce “Mun bukaci babban mai shari’a na tarayya da gwamnan babban bankin Najeriya CBN da su mutunta umarnin kotun koli na wucin gadi wanda har yanzu ake ci gaba da aiki. Cewa taron yana kira ga mai girma shugaban kasa da ya sa baki wajen warware matsalolin da ke jawo wa al’umma wannan babbar matsala da tattalin arziki.”

A halin da ake ciki kuma, a cikin sa’o’i na ganawar sirrin, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, ya mamaye sakatariyar jam’iyyar.

An boye bayanan zuwan sa gidan Buhari domin ya ki yin jawabi ga manema labarai.

Taron ya samu halartar gwamnan jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai; Mohammed Bello of Niger, Abdulahi Sule of Nasarawa, Yahaya Bello of Kogi state, Inuwa Yahaya of Gombe state, Bello Matawalle of Zamfara , Mai Mala Buni of Yobe, Abubakar Badaru of Jigawa , Biodun Oyebanji of Ekiti, Simone Lalong of Plateau, Atiku Bagudu na jihar Kebbi, Babajide Sanwolu na jihar Legas, da mataimakan gwamnonin jihar Imo, Placid Njoku, da Mohammed Manir Yakubu na jihar Katsina.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here