Dole ne Shugabannin PDP su Haɗa Kansu – Atiku Abubakar

 

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, yace dole ne shugabannin PDP su haɗa kansu.

Atiku yace bai kamata ana samun irin wannan hatsaniyar a dai-dai wannan lokacin ba kuma a cikin PDP Hakanan.

Atiku ya musanta zargin cewa yana da hannu a kitsa rikicin dake karuwa.

Abuja:- Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya yi kira ga shugabannin PDP da su haɗa kansu domin cigaban jam’iyyar da kasa baki ɗaya.

Atiku ya yi wannan kiran ne a wata sanarwa da kakakinsa, Paul Ibe, ya fitar ranar Alhamis a Abuja yayin da yake martani kan sabon rikicin da ya kunno.

Punch ta rahoto Atiku yace PDP ba zata yarda a raba ta a dai-dai lokacin da yan Najeriya ke Allah-Allah su samu canjin gwamnati.

Atiku yace a matsayinta na jam’iyyar adawa ya kamata ta gaggauta nemo hanyar warware matsalar domin bai kamata a zuba wa jam’iyya mai mulki ido tana cin karenta babu babbaka.

Dagaske ne Atiku na cikin masu rura wutar rikicin?

Tsohon mataimakin shugaban kasan ya musanta zargin da ake masa cewa yana da hannu a wajen rura wutar rikicin dake faruwa a PDP.

Atiku ya kara da cewa bada jimawa ba yana daga cikin waɗanda suka jagoranci sulhu a faɗin kasar nan kuma ya yi imanin ta wannan hanyar ne kaɗai komai zai dai-daita, kamar yadda vanguard ta ruwaito.

Wani sashin jawabin yace:

“Jam’iyyar PDP ta zarce bukatun mu na kai da kai, ya kamata mu kintsa kanmu kafin mu fara maganar muradin mu. Wajibi ne mu kula sosai domin kome muka yi jam’iyya mai mulki tana kallo.”

“Ba zamu bari jam’iyya ɗaya ta cigaba da mulkin Najeriya ba domin hakan zai sa fatan mutane na samun canji a 2023 ya bi iska.”

Menene babbar matsalar da hanyar magance ta?

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa karkashin PDP ɗin ya yi gargaɗin cewa rashin haɗin kai da amincewa juna zai taimakawa jam’iyya mai mulki fiye da PDP.

Ya kara da cewa mai son Najeriya ta cigaba da kasancewa a halin da take ciki ne kaɗai zai so rikicin PDP ya ɗore.

Atiku yace ya zama wajibi jiga-jigan PDP su jingine duk wani banbanci gefe guda su yi aiki tukuru domin goben jam’iyya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here