An Tashi Bam a Babban Birnin Somalia

Rahotanni sun ce wani ɗan ƙunar bakin wake ya kai hari kan ababan hawan da ke wajen binciken motoci a babbar hanyar zuwa filin jirgin saman Aden Adde.

Wasu majiyoyi daga wajen da lamarin ya faru sun ce harin ya raunata mutane da dama ciki har da sojoji da fararen hula.

Wajen da aka kai harin na da nisan kilomita biyar ne daga filin jirgin saman, kuma anan ne ake ganin ‘yan takarar shugabancin kasar za su gudanar da jawabai a game da takararsu.

Tuni aka sanya dokar takaita zirga-zirga a wuraren da za a gudanar da zaben shugaban kasa a Ranar Lahadi mai zuwa.

‘Yan takara 39 ne ke neman kujerar shugabancin kasar wanda aka jinkirta shi saboda yanayin tsaro a kasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here