Tattalin Arziki: Kwamitin Majalisar Dattawa ta Fara Tattaunawa da Shugaban Babban Bankin Najeriya

 

Kwamitin hadin gwiwa na Majalisar Dattawa mai kula da harkokin kudi da Banki da Inshora da cibiyoyin hada-hadar kudi na Najeriya ya fara tattaunawa da jami’an babban bankin Najeriya (CBN) da Gwamnan bankin Yemi Cardoso ke jagoranta.

A ranar 31 ga watan Janairu ne dai kwamitin ya gayyaci gwamnan babban bankin kasar ya bayyana a gabansa.

Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da ake nuna damuwa kan halin da tattalin arzikin ƙasar ke ciki da kuma faduwar darajar Naira a kasuwar canji.

Sanatocin sun bukaci babban bankin kasar na CBN ya yi bayani kan dimbin kalubalen tattalin arzikin da kasar ke fuskanta a halin yanzu.

Kasancewar talauci da rashin tsaro a kodayaushe sakamakon matsalar karancin abinci a ƙasar, ‘yan majalisar sun yi imanin cewa CBN ba zai iya gamsar da ‘yan Najeriya cewa manufofinsa suna aiki ba.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com