Nuhu Ribadu

Tsohon shugaban hukumar EFCC, Nuhu Ribadu ya yai kira ga gwamnonin kasar nan na su yi koyi da irin halayyar Buhari a wajen mulkin mutanen jihohin su.

Ribadu yayi wannan kira a wajen taron wanke sabbin gwamnoni da ma tsoffi da kayi a Abuja.

” Ku duba ku gani, irin halayyara shugaba Muhammadu Buhari, bashi da wasu abokanai wai ‘yan kasuwa da za ace wai kullum suna tare dashi a ana shirya harkalla. Sannan yadda ya soma a 2015 haka yake har yanzu, bai siya ba kuma bai gina ba.

” Kun gani yanzu lokacin zama attajiri farad daya ya wuci a dalilin salon mulkin Buhari. Aiki dabam, wasa da bam.”

A tsokaci da yayi game da dalilan da ya sa hukumomin binciken ta kasa ke bibiyar gwamnoni, Ribadu ya ce “Ku ne ke da hakkin tafiyar da gwamnatin ku. Ku ne kuma ke rike da komai na dukiya, albarkatu da makudan kudaden jiha, har ma da na kananan hukumomi.” Cewar Ribadu.

Ya yi wannan tsinkaye ne a lokacin da ya ke jawabi wurin taron sanin makamar aiki da aka shirya wa zababbun gwamnoni, jiya Talata, a Abuja.
Daga nan sai Ribadu ya nanata cewa babu yadda za a yi a ce gwamnoni ba a bincike su ba.

Ya ce kai hatta ma wanda suka zabo da kan su domin ya gaje su, zai iya binciken su, kamar yadda tarihi ya nuna ba da dadewa ba a baya.

Daga nan sai Ribadu ya ce jami’an tsaro na duniya su na bibiyar duk lunguna da sako-sakon da kudade ke shiga, saboda yawaitar safarar muggan kwayoyi, ta’addanci da ya buwayi duniya da kuma shugabanni masu wawurar kudade.

Daga

Premium Times

The post Ya kamata Gwamnoni su yi koyi da Buhari -Ribadu appeared first on Daily Nigerian Hausa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here