Ƴan Bindiga Sun yi Garkuwa da Manoma a Jihar Neja

 

Rahotanni daga jihar Neja a Najeriya na cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da manoma a wani ƙauye da ke karamar hukumar Paikoro.

Wasu daga cikin mazaunan ƙauyen na Kaffin-Koro sun shaida wa manema labarai cewa ‘yan bindigan sun shafe tsawon sa’o’i suna cin karensu babu babbaka, lamarin da ya tilasta wa mutane da dama tserewa.

An kai hari ne a ranar Labara a yankuna da dama da ke ƙauyen, sannan akwai mutum ɗaya da aka kashe.

Babu dai wasu cikakkun bayanai kan adadin manoman da aka yi garkuwa da su, sai dai yankin Neja na daga cikin yankunan Najeriya da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga domin neman kudin fansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here