‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Coci Sun yi Garkuwa da Mutane 25 a Kaduna

 

Wasu `yan bindiga sun kai hari kan wani Coci da ke karamar hukumar Chikun a jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya inda suka sace mutum akalla 25.

Lamarin dai ya auku ne a ranar Lahadin da ta wuce lokacin da mutanen suke ibada a Cocin.

Shugaban kungiyar Kiristocin Najeriya reshen jihar Kaduna, Reverend John Hayap ya tabbatar wa BBC aukuwa lamarin inda ya ce mutum 40 aka sace kafin daga bisani mutum 15 sun kubuta.

Kakakin rundunar `yan sanda a jihar Kaduna, ya tabbatar wa da kamfanin dillancin labarai na AFP aukuwar lamarin amma bai yi karin bayani ba a kan batun.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here