‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Bijilanti 2 a Abuja

 

Yan bindiga da suka yi garkuwa da wani manomi sun halaka jami’an tsaro na bijilanti biyu a birnin tarayya Abuja.

Yan bijilanten sun tafi sansanin yan bindigan ne da nufin ceto wani Aliyu Musa da aka sace daga gonarsa amma yan bindigan suka musu kwanton bauna.

Wani dan bijilante da ya ce sunansa Ishaku ya ce lamarin ya faru ne misalin karfe 4.30 na yammacin Alhamis kuma an yi wa wadanda suka rasu jana’iza.

Abuja- Wasu mambobin kungiyar bijilante biyu sun mutu sakamakon gumurzu da suka yi da yan bindiga a garin Gasakpa a gundumar Gawu, karamar hukumar Abaji, Abuja, rahoton Daily Trust.

Wani mamban kungiyar yan bijilante mai suna Ishaku ya ce lamarin ya faru ne misalin karfe 4.30 na ranar Alhamis a wani daji da ke kan iyakar Abuja da jihar Niger.

Ya ce yan bijilanten sun tafi dajin ne domin ceto manomi mai suna Aliyu Musa wanda aka sace shi a gona.

Isiyaku ya ce yan bijilanten suna daf da isa sansanin yan bindigan ne kwatsam suka bude musu wuta.

A cewarsa, an kashe mutum biyu cikin yan bijilanten sakamakon musayar wuta da suka yi, yana cewa an musu jana’iza.

Martanin yan sanda

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar, DSP Adeh Josephine, bata riga ta amsa sakon tes da aka aika mata ba game da lamarin.

Daily Trust ta rahoto cewa a baya-bayan nan, yan ta’addan sun rika kai hare-hare a garuruwan Adagba, Gurdi, Paiko Bassa da Rafin Daji a karamar hukumar Abaji da ke da iyaka da kauyukan Jihar Niger.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here