Jam’iyyar Adawa a Chadi ta Soki Tsawaita Mulkin Mahamat Deby

 

Babbar jam’iyyar adawa ta kasar Chadi ta bayyana rantsar da jagoran mulkin soji na kasar Mahamat Idriss Deby na karin shekara biyu a matsayin wata koma-baya ga mulkin demokradiyya.

Mataimakin shugaban kungiyar da ake kira “The Transformers”, masu neman kawo sauyi, Ndolembai Njesada, ya kuma soki damar da aka bai wa Mahamet Deby na yin takara a zaben kasar mai zuwa.

Ya bayyana cewa wannan tamkar an bai wa shugaban wuka da nama ne.

Mr Njesada ya kuma yi barazanar kafa gwamnati ta daban a kasar.

Manyan kungiyoyin ‘yan adawa na kasar da ‘yan tawaye sun ki shiga tattaunawar da aka gudanar, wadda a lokacin ne aka amince da tsawaita mulkin Shugaba Deby.

A bara ne Mahamat Deby ya karbi mulki bayan kisan da aka yi wa mahaifinsa a fagen daga.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here