An gurfanar da mutum uku a gaban kotun kasar Zimbabwe in da ake zarginsu da satar jakar tsohon shugaban kasar, Robert Mugabe, wadda ke dauke da $150,000 (kimanin Naira Miliyan 54).

Wadanda ake zargin, sun kashe kudaden ne a kan sayen motoci, gidaje da kuma dabbobi.

‘Yar uwar tsohon shugaban, Constantia Mugabe, na daga cikin wadanda ake zargin.

Ana zargin tana da makullan gidansa da ke a kauyen Zvimba a kusa da babban birnin kasar, Harare, in da ta bai wa sauran mutanen makullan.

Sauran wadanda ake zargin masu hidimomin gida ne a lokacin da aka yi satar wadda ta auku tsakanin 1 ga watan Disamba na 2018 zuwa Janairu.

Robert Mugabe ya jagoranci kasar na tsawon shekara 37, in da wasu ke zarginsa da kwashe kudaden kasar domin jin dadin kansa.

A shekarar 2017 ne sojojin kasar suka hambare Robert Mugabe mai shekara 94.

BBC Hausa

The post An sace jaka cike da daloli a dakin Robert Mugabe appeared first on Daily Nigerian Hausa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here