Samar da Danyen Mai: Angola da Libya Sun Shiga Gaban Najeriya – OPEC

 

Adadin danyen man fetur da Najeriya ke samarwa ya yi kasa zuwa ganga 972,000 a duk rana a cikin watan Agusta, wanda hakan yasa kasashen Angola da Libya suka shiga gabanta wurin samar da danyen man a watan.

Hakan na kunshe ne a rahoton da kungiyar kasashe masu arzikin man fetur (OPEC) ta fitar a cikin watan Satumba.

Wannan ne karon farko a cikin shekaru da dama, da Najeriya ta samar da ganga kasa da miliyan daya ta danyen man fetur a rana.

Kazalika rahoton na OPEC ya ce lamarin ya sa kasashen Angola da Libya sun sauko da Najeriya wurin samar da danyen man fetur a dan tsakanin.

Rahoton ya ce ” fitar da danyen mai ya karu a kasashen Libya da Saudi Arabia, yayin da ya ragu a Najeriya.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here