Bam ya Fashe a Babban Birnin Jihar Taraba

 

Mutane a birnin Jalingo na jihar Taraba sun shiga firgici, bayan wani abin fashewa ya fashe a birnin.

Abin fashewar wanda ake kyautata zaton bam ne ya fashe ne dai a wata matsaya da ke cikin birnin na Jalingo.

Ba a samu asarar rayuka ba, amma mutane da dama sun samun raunika, inda aka garzaya da su zuwa asibiti.

Jihar Taraba – Wani abin fashewa wanda ake kyautata zaton bam ne, ya fashe a daren ranar Lahadi a Jalingo, babban birnin jihar Taraba.

Jaridar Tribune ta kawo rahoto cewa lamarin ya auku ne a wajen wata mashaya a Doruwa kusa da bankin Polaris, sannan ya shafi wasu gine-gine a yankin, yayin da mutane da dama waɗanda ba a san yawansu ba, suka samu raunika.

Channels Tv ta yi rahoto cewa wata budurwa ta samu mummunan rauni, inda aka garzaya da ita wani asibiti wanda ba a bayyana sunansa ba.

Ba a samu asarar rai ba a tashin bam ɗin, sai dai mutane da dama da suka samu raunika a dalilin fashewarsa.

Tuni jami’an ƴan sanda masu hana tashin bam suka zagaye wajen domin hana aukuwar tashin wani bam ɗin, idan har ta yiwu an dasa wani bam ɗin a kusa da wajen.

Tashin bam ɗin da ya auku a Doruwa, shine na huɗu da ya taɓa aukuwa a babban birnin jihar tun shekarar 2022, sannan na biyar da ya auku a jihar tun shekarar 2022.

Gwamnatin jihar Taraba da jami’an tsaro ba su fitar da wata sanarwa ba, dangane da wannan lamarin har ya zuwa lokacin kammala haɗa wannan rahoton.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here