Majalisar Wakilai za ta Binciki Musabbabin Hauhawar Kayan Abinci a Najeriya

 

Majalisar wakilai a Najeriya ta ce za ta binciki musabbabin hauhawar kayan abinci a kasar.

Honorabul Adekunle Isiaka daga jahar Ogun ne ya gabatar da bukatar a gaban majalisar a zamanta na yau Laraba, inda ya ce “mafi yawan yan Najeriya ta kai ga ba sa iya sayen abincin da za su ci a rana, lura da cewa farashin kayan abincin da na gas ya ninka daga bara zuwa bana.”

A kan haka ya bukaci Shugaban majalisar Femi Gbajabiamila da ya kafa kwamitin da zai binciko inda matsalar take kafin tafi karfin magancewa.

Kayan abinci sun yi tashin gwauron zabi musamman a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya, inda aka rufe kasuwannin mako-mako saboda shawo kan matsalar tsaro.

Kazalika gas din dafa abinci ya ninka daga kasa da naira 4,000 zuwa naira 7,000 a tukunya mai nauyin kilo 12.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here