Shugaba Buhari ya yi Sabon Nadi a Hukumar Tattara Haraji na Tarayya

 

Shugaba Muhammadu Buhari yana son ganin komai ya daidaita a kasar kafin ya karewar wa’adinsa a watan Mayu.

Ana makonni kadan kafin babban zaben shekarar 2023, Buhari ya yi nadi mai muhimmanci a hukumar tattara haraji na tarayya, FIRS.

Watanni hudu kafin karewar wa’adinsa, shugaban na Najeriya ya nada Mr Lawal Sani Stores a kwamitin hukumar FIRS.

FCT, Abuja – Shugaba Muhammadu Buhari ya nada Mr Lawal Sani Stores a matsayin mamba a kwamitin Hukumar Tattara Haraji na Kasa, FIRS.

Wannan nadin na kunshe ne cikin wata sanarwa da aka fitar a birnin tarayya, Abuja, ranar 9 ga watan Janairu, ta hannun Tanko Abdullahi, mashawarci na musamman kan watsa labarai da sadarwa na ministan kudi, kasafi da tsare-tsaren kasa, Mrs Zainab Ahmed.

Sabon wanda aka yi wa nadin da dalilin da yasa Buhari ya nada shi

Stores zai maye gurbin Ado Danjuma ne, wanda ke wakiltan Arewa maso Yamma, kuma a baya-bayan nan aka nada shi matsayin babban direkta na Hukumar Tsaro da Buga Takardun Kudi na Kasa, Vanguard ta rahoto.

A cewar sanarwar, nadin ya zama dole ne don cike gurbin da Mr Ado ya tafi ya bari.

Bayanai game da Stores

An haifi shi ne a ranar 11 ga watan Maris na 1956 a Katsina, Jihar Katsina.

Ya yi babban diploma ta kasa (HND) a bangaren kasuwanci daga Kwalejin Kasuwanci da Fasaha ta West Bromwich da ke Ingila.

Ya kuma tafi Jami’ar Bayero ta Kano, inda ya yi karatun PGD a Management da digiri ta biyu a bangaren kasuwanci (MBA) a harkar kasuwanci da saka hannun jari.

Sabon mamban na kwamitin FIRS ya shafe akalla shekaru 30 yana aiki kuma ya kware a bangarori daban-daban da samun horaswa a bangarori daban-daban, Leadership ta rahoto.

An kuma ce ya halarci tarukan kara wa juna ilimi daban-daban da kwasa-kwasai a gida da waje.

Mr Stores ya kasance mamba a kwamitocin hukumomi daban-daban kamar SEC, CIS, Greenwich Trustees Limited da PenCom.

Buhari ya yi nadin mukami a ma’aikatar sadarwa da tattalin arzikin zamani

A wani rahoton, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yarda da nadin Hon Adepoju Adeyemi Sunday a matsayin babban shugaban aika (PMG) na Hukumar Aika Sakonni ta Najeriya (NIPOST). Kafin nadinsa, Honarabul Sunday tsohon mamba ne na majalisar wakilai na tarayya.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here