ƙasar Chadi na Shirin Tura Sojoji Dubu 1 Zuwa Mali  

 

Ma’aikatar harkokin wajen Mali ta bayyana cewa ƙasar Chadi na shirin tura mata ƙarin sojoji dubu domin taimaka mata yaƙi da masu iƙirarin jihadi a daidai lokacin da Faransa ke rage yawan sojinta a ƙasar.

Sojojin da ke mulkin Mali sun yi murna da wannan matakin na Chadi.

Ana dai kallon sojojin Chadi a matayin waɗanda ke ƙoƙari a yaƙi da masu iƙirarin jihadi.

Wannan yunƙurin na gwamnatin Chadi na zuwa ne a daidai lokacin da Faransa ke ƙoƙarin shawo kan sauran ƙasashen duniya domin kai sojoji yankin Sahel.

Tuni Faransa ta rufe sansanoni uku na sojinta da ke Mali a bana haka kuma nan da watanni masu zuwa za ta janye wasu dakarunta dubu 5000.

Sakamakon irin ƙarin hare-haren da ake samu a Mali da Burkina Faso da Nijar, mutane na ƙara saka ayar tambaya kan tasirin ƙasashen waje a yaƙi da masu iƙirarin jihadi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here