Za a Ci gaba da Harkokin Zirga-Zirgan Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna Cikin Watan nan – Ministan Sufuri

 

Abuja – Ministan sufuri, Mu’azu Sambo, ga bayyana cewa a wannan watan na Nuwamba da mukee ciki ake shirin ci gaba da harkokin zirga-zirgan Jirgin ƙasa a layin dogon Kaduna zuwa Abuja.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa ba ya ga haka, gwamnati ta shirya sintirin tsaro a layin dogon na tsawon awanni 24 kowace rana da nufin kare sake kai hari.

Ministan ya sanar da haka ne a babban birnin tarayya Abuja yayin da yake zayyana ayyukan ma’aikatar sufuri tun daga shekarar 2015 zuwa yau.

Yace sun shirya ingantaccen kuma isasshen tsaro domin tabbatar da tsare rayukan fasinjoji amma bai faɗi ainihin ranar da zirga-zirgan jirgin ƙasan zata ci gaba ba.

Sambo ya ƙara da cewa ma’aikatar Sufuri ta ɗauki darasi a harin da ‘yan ta’adda suka kai a watan Maris, wanda ya haddasa dakatar da Sufurin jirgin ƙasa a Titin Kaduna-Abuja.

Ministan ya sanar da cewa a yanzun an sanya wasu na’uroro a Layin dogon domun sa ido kan duk wata halitta da zata gitta a kan titin, kamar yadda Channels tv ta ruwaito.

A cewarsa, na’urar zata bai wa shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ma’aikatu da sauran ɓangarorin da lamarin da shafa da ma hukumomin tsaro damar ganin abinda ke wakana a kan titin ba tare da jinkiri ba.

Ku dakaci karin bayani…

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here