Wani dalibi a wata karamar makarantar sakandire da aka sakaya sunanta a jihar Abiya ya dirkawa wata budurwa mai yiwa kasa hidama karkashin NYSC cikin shege.

Lamarin dai ya janyo cece kuce a makarantar ta yadda akai mai yiwa kasa hidamar har ya bari dan aji uku na karamar sakandire yayi kwance kwance ya dirka mata ciki.

Wasu da dama na ganin duba da yadda ‘yar yiwa kasa hidimar ta baiwa dalibin tazarar shekaru bai kamata ace ya bari hakan ya auku tsakaninsu ba, yayin da wasu ke tunanin ko barazana dalibin ya yiwa budurwa.

Ana dai cigaba da gudanar da bincike domin gano bakin zaren matsalar da yadda za a warware ta.

The post Dalibi dan JSS 3 ya dirkawa wata ‘yar bauta kasa cikin shege appeared first on Daily Nigerian Hausa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here