Malam Salihu Sagir Takai ya bayyana dalilan da suka sanya ya fice daga cikin jam’iyyar PDP zuwa sabuwar jam’iyyarsa ta PRP da ya yanki katin shigarta a ranar Alhamis.

Takai ya bayyana cewar rashin adalcin da aka yi musu a PDP bayan sun cika dukkan ka’ida da dokokin shiga zabe amma aka tauye musu hakki.

”A bisa doka da ka’idar jam’iyya dole a sanar da dan takara awa 48 kafin yin zaben fidda gwani na jam’iyya sannan a bashi sunayen wakilan da zasu gudanar da zabe, amma babu ko daya da aka yi, kawai muka ji labarin wai anyi zaben fidda gwani na PDP a gidan wani mutum”

”Mun rubuta korafi tare da kokenmu ya uwar jam’iyyar PDP ta kasa akan a bi mana hakkinmu bayan mun bi dukkan ka’idoji, amma uwar jam’iyya ta gaza yi mana adalci a wannan halin “

”A sabida haka muka yanke shawarar sallama jam’iyyar PDP dan haka muka nutsu tare da gamsuwa da jam’iyyar PRP kuma muna fatan Allah ya bamu Nasara” A cewar Malam Salihu Sagir Takai.

The post Dalilan da suka sanya na koma jam’iyyar PRP – Takai appeared first on Daily Nigerian Hausa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here