Allah ya yi wa Ɗan Takarar Majalisar Wakilai na NNPP a Kano  Rasuwa

 

Ɗan takarar kujerar majalisar wakilai a karkashin jam’iyyar NNPP a mazaɓar Wudil da Garko a jihar Kano, Kamilu Ado Isa ya rasu.

Ya rasu ne a jiya Lahadi bayan fama da gajeriyar rashin lafiya.

Hakan na zuwa ne ƙasa da mako guda kafin babban zaɓen Najeriya na 2023.

Ado Isa ya kasance tsohon mataimakin kontrola-janar na hukumar tsaron farin kaya na Civil Defence.

NNPP dai na cikin manyan jam’iyyun siyasa da ake hasashen za su iya taka rawar gani a zaɓen da ke tafe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here