Kotun Ecowas ta Umarci Sojojin Nijar da su Saki Mohammed Bazoum

 

Kotun Ecowas ta umarci sojojin Nijar da su gaggauta sakin Mohammed Bazoum da suka tsare tun daga ranar 26 ga watan Yuli da suka hamɓarar da shi.

Kotun ta nemi a gaggauta sakin sa ba tare da wani sharaɗi ba sannan a mayar da Bazoum kan kujerarsa, kamar yadda alƙalin kotun ya faɗa a ƙarar da aka saurara a Abuja, babban birnin Najeriya.

A ranar Alhamis ne ƙungiyar ta Ecowas ta sanar da cikakkiyar dakatarwar da ta yi wa Nijar sanadiyyar juyin mulkin.

A baya, wasu ƙasashe mambobin ƙungiyar sun yi watsi da hukuncin kotun ta Ecowas.

“Mohamed Bazoum ne yake wakiltar Nijar … kuma har yanzu shi ne shugaban Jamhuriyar,” kamar yadda hukuncin kotun ya bayyana.

“Akwai haƙƙoƙin da aka take.” An tsare Bazoum a gidansa na shugaban ƙasa tare da mai ɗakinsa da ɗansu tun lokacin da aka tsige shi.

A tsakiyar watan Satumba ne, hamɓararren shugaban ya nemi kotun ta Ecowas ta bayar da umarnin sakin shi tare da mayar da ƙasar kan turbar dimokraɗiyya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com