Ecowas ta yi Allah Wadai da Garkuwa da Yara 80 a Arewacin Najeriya

Kungiyar Tattalin Arzikin ƙasashen Afirka ta yamma ECOWAS ta yi Allah wadai da garkuwa da yara 80 a arewacin Najeriya cikin makon da ya gabata.

Mafi yawan waɗanda aka yi garkuwa da su a jihar zamfara da ke arewa maso yammcin ƙasar, mata ne da yara waɗanda suka je sharar gona da yin itace a daji.

A wata sanarwa ECOWAS ta yi kira da a saki yaran. Kawo yanzu dai babu wanda ya ɗauki alhakin sace yaran.

Harin dai shi ne na baya-bayan nan a jihar , wadda ke fama da yawaitar hare-haren ‘yan bindiga masu sace mutane domin neman kuɗin fansa.

A makon da ya gabata ma fiye da mutum 70 aka kashe a wasu tagwayen hare-hare a jihar Benue da ke tsakiyar ƙasar.

A ranar Juma’a kuma wasu ‘yan bindigar suka kashe gwamman ‘yan gudun hijira bayan da suka kai wa sansaninsu hari.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here