Shugabannin Fansho na karkatar da kuɗaɗen Jama’a a Najeriya – EFCC
Shugaban hukumar EFCC Abdulrasheed Bawa ya ce shugabannin kamfanonin fansho na karkatar da bilyoyin kudaden mutane a Najeriya.
Ya shaida hakan ne a taron kwanaki biyu da ya ke halartar kan kawar da rashawa a tara kuɗaɗen fansho a Najeriya.
Bawa ya ce EFCC da ke yaƙar rashawa tana sane da irin aika-aika da ake aikatawa da kuɗaɗen fanshon mutane.
A cewarsa bincikensu ya nuna musu yada ake tafka rashawa a fanin fansho wanda hakan abin kunya ne ga kasa.
Ya kuma shaida cewa gwamnati na duba batun domin ganin ta samar da mafita da hukunta masu tauye hakkin mutane.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here