Masu Garkuwa da Mutane Sun yi Awon Gaba da Manoma a Jihar Osun

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da wasu manoma biyu a yankin Ileogbo da ke jihar Osun.

Jaridar Premium Times a Najeriya ta ce an sace manoman a ranar Laraba lokacin da suke dawowa daga gonakinsu.

Wata majiyar tsaro da ta bukaci a sakaya sunanta ta ce manoman na tafiya ne tare da wasu mutane bakwai a lokacin da masu garkuwan suka far wa motar su a unguwar Oke Osun da ke Ileogbo.

Majiyar ta ci gaba da cewa sauran bakwai da aka kashe sun tsere amma masu garkuwan sun tafi da manoman biyu.

Wata majiya mai tushe wacce kuma ta nemi a sakaya sunanta saboda dalilan tsaro ta ce masu garkuwan sun tuntuɓi iyalan wadanda aka kashe a ranar Alhamis inda suka bukaci a biya su fansar naira miliyan 10.

Kwamandan jami’an tsaro na Amotekun a jihar Osun, Amitolu Shittu ya tabbatar da faruwar lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here