Gwamnan Katsina ya Fadi ta Inda ‘Yan Bindiga Suke Shigowa Jahar

 

Yan bindiga na ta’asa a Katsina sannan su tsere zuwa Zamfara don buya.

Wannan shine matsayar Gwamna Bello Masari na jihar Katsina.

Masari ya kara da cewa kimanin 99% na miyagun da ke garkuwa da mutane, kisa da sata a jiharsa sun fito ne daga Zamfara.

Gwamnan jihar Katsina, Bello Masari, a ranar Litinin, 16 ga watan Nuwamba, ya koka kan ayyukan yan bindiga a jiharsa.

Masari, wanda ya yi magana da manema labarai a Kafur ya bayyana cewa mafi akasarin wadannan miyagun su kan je su haddasa tashin hankali a Katsina sannan su koma mabuyarsu a Zamfara, jaridar The Nation ta ruwaito.

Gwamnan ya yi korafin cewa yan bindigan na yin duk abunda za su iya don wargaza kokarinsa na dawo da zaman lafiya, tsaro da oda a Katsina.

Ya yi kira ga rundunar sojin Najeriya da taimakon sauran hukumomin tsaro da su abunda za su iya domin fitar da yan bindigan.

Gwamnan ya ce: “Wuraren da muke da matsala kawai sune kananan hukumomin Faskari, Sabwa da Dandume a jihar, a yankunan Jibia, Batsari, Safana da Danmusa an samu zaman lafiya.

“Daga rahotannin, da nake samu duk safe idan ka ga lamarin fashin shanu ko garkuwa da mutane toh yawacinsu a kewayen Faskari, Sabwa da Dandume ne. Muna ta kai wa hukumar soji korafi a kan su karbe ragamar yankunan Gurbi-Gidan Jaja-Kaura Namode na jihar Zamfara.

“Har sai an dawo da cikakken tsaro a wannan yankuna, kasancewarsu masu hatsari inda yawancin yan bindiga ke zama da yawo kai tsaye, idan ba haka ba, ba za mu iya kare Katsina ba ba tare da tsaro a Zamfara ba, saboda kaso 99 na dukkanin hare-hare da garkuwa da mutane da ke faruwa a Katsina daga Zamfara ne.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here