Somalia: An Kai Harin Bom Kusa da Fadar Shugaban Kasa a Mogadishu
Wata mota makare da bama -bamai ta tashi kusa da fadar shugaban kasa a Mogadishu, babban birnin Somalia.
Read Also:
Kafafen yada labarai na cikin gida sun ce an kai harin ne a dogon jerin motoci a wani shingen bincike na jami’an tsaro.
An samu rahotannin da ke cewa mutane sun mutu kuma wasu sun jikkata.
Kungiyar masu kishin Islama ta Al Shabaab ta ce ita ta kai harin.
Kungiyar ke da iko da manyan yankuna na kudanci da tsakiyar Somalia kuma a kai a kai tana kai hare-hare a yankunan da ke karkashin ikon gwamnati, musamman ma Mogadishu.