Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Matar da Take Satar Kananan Yara

Wata kotu a birnin Beira na kasar Mozambican ta yanke wa wata mata hukuncin daurin shekara 30 a gidan yari, da kuma biyan tarar dala 3,100, sakamakon samunta da laifin sace wasu kananan yara guda biyu domin neman kudin fansa.

A watan Oktoban bara ne matar mai shekara 37, ta sace wani yaro mai shekarar 14, inda ta nemi kudin fansa kusan dala 313.

Haka kuma ta kara sace wani yaron a watan Disamba, inda ta nemi kudin fansa dala 390.

Alkalin kotun ya ce ”Abu guda daya da za a yi domin kawar da aikata irin wannan laifi, shi ne zartar da hukuncin da doka ta tanada a kan duk wanda ya aikata makamancinsa”.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here