Kaduna: Gwamnatin ta Saka Dokar Hana Fita a ƙaramar Hukuma Biyu

Gwamnatin Jihar Kaduna ta saka dokar hana fita a wasu yankuna na ƙananan hukumomin Kaduna ta Kudu da kuma Chukun na jihar ta tsawon awa 24.

Dokar za ta yi aiki ne a unguwannin Barnawa da Kakuri da Television, waɗanda ke Kaduna ta Kudu.

Sai kuma Maraban Rido da Sabon Tasha da Narayi da Unguwan Romi da ke Chukun.

Wata sanarwa da Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida Samuel Aruwan ya fitar ta ce dokar za ta fara aiki ne nan take.

Aruwan ya yi kira ga mazauna jihar da su guji tayar da tarzoma da kauce wa faɗawa tarkon masu tayar da husuma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here