An Kama Direban Da ke Mika Fasinjoji Hannun Masu Garkuwa a Kano
‘Yan sandan Najeriya sun kama wani direban motar haya da ake zargi da yaudarar fasinjoji zuwa wurin masu garkuwa da mutane a Jahar Kano da ke arewacin Najeriya.
Rahoton jaridar Daily Trust ya bayyana matashin mai shekara 25 a matsayin ɗaya daga cikin wani gungun mutum 11 da ke aikata garkuwa da mutane.
Read Also:
Yayin da ake gabatar da su ga manema labarai a Abuja ranar Talata, ‘yan sanda sun ce gungun ya ƙunshi maza tara da mata biyu, waɗanda ke gudanar da ayyukansu a tashoshin mota biyu da ke Kano.
Kakakin rundunar ‘yan sanda ta Najeriya Frank Mba ya ce dakarunsu sun yi nasarar ƙwace bindigar Ak-47 biyu da harba-ruga biyu da kuma wasu makaman daban daga hannunsu.
“Nakan hau motar a matsayin fasinja, wani lokacin kuma na tuƙa tawa motar,” a cewar Bashiru Sule, ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin.
“Ina yin lodi a tasha sannan kuma na faɗa wa masu garkuwa da mutanen labarin mutanen da na ɗebo a motar.”