An Kama Magoya Bayan Arsenal Kan Murnar Nasarar Doke Abokiyar Hamayyarta Man United

 

Aƙalla magoya bayan ƙungiyar Arsenal takwas aka kama a birnin Jinja na kasar Uganda, sakamakon murnar nasarar da ƙungiyar ta yi kan babbar abokiyar hamayyarta Manchester a wasan Premier League da suka buga ranar Lahadi.

Magoya bayan – waɗanda ke sanye da jajayen rigunan ƙungiyar – na riƙe da wani abu da ke alamta kofin Premier.

‘Yan sanda sun ce mutanen ba su da izinin gudanar da gangamin, kuma yin hakan laifi ne a ƙasar.

Arsenal ta samu nasara a kan abokiyar hamayyarta Manchester United da ci 3-2 a wasan na ranar lahadi.

Sakamakon ya bai wa ƙungiyar tazarar maki biyar a saman teburin Premier, lamarin da ya bai wa magoya bayanta a faɗin duniya ƙwarin gwiwwar ɗaukar kofin Premier karon farko cikin shekara 19.

‘Yan sanda sun kama magoya bayan – waɗanda ke cikin jerin gwanon motoci ranar Litin da safe – inda ɗaya daga cikinsu ke riƙe da kofin da suka haɗa kuɗi suka saya a wani shago a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here