An Samu ƙarancin Masu Kaɗa ƙuri’a a Kaduna

 

Rahotonni daga jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya sun ce an samu ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a a zaɓen gwamna da na ƴan majalisar dokoki da ake gudanarwa a jihar.

Bayanai sun nuna cewa tun misalin ƙarfe 8:30 na safe aka fara kaɗa ƙuri’a a wasu sassan birnin.

A mafi yawan rumfunan zaɓen da BBC ta ziyarta a cikin birnin Kaduna an ga ƙarancin fitowar mutane domin kaɗa ƙuri’a, ba kamar yadda aka gani a zaɓen shugaban ƙasar da ya gabata ba, inda mutane da dama suka fito.

Wani mai kaɗa ƙuri’a mai suna Malam Baba ya shaida wa BBC cewa a mazaɓarsa da ke unguwar Kawo mutane ƙalilan ne suka fito zaɓe.

Ya kuma ce babu mata sosai a rumfar zaɓen nasa.

A sassan ƙasar da dama dai rahotonni na cewa mutane ba su fito zaɓen ba kamar yadda suka fita zaɓen shugaban ƙasa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here