Kotu ta ba da Belin ɗan Majalisar Wakilan Tarayya, Honorabul Farah Dagogo

Rivers – Bayan kwashe kwanaki 62 a garkame, Babbar Kotun jihar Ribas karkashin jagorancin Mai Shari’a Chinwendu Nworgu ta amince da buƙatar ba da Belin ɗan majalisar wakilan tarayya, Honorabul Farah Dagogo.

Ledership ta ruwaito cewa Dagogo,wanda ya nemi takarar gwamna a jam’iyyar Peoples Democratic Party wato PDP, na fuskantar shari’a ne kan zargin aikata babban laifi.

Ɗan majalisar ya shiga hannun hukumomi ne a ranar 22 ga watan Afrilu, 2022 a wurin taron tantance yan takarar gwamnan na jam’iyyar PDP wanda ya gudana a Patakwal.

An kama shi ne ƙasa da awanni huɗu bayan gwamna Nyesom Ezenwo Wike na jihar Ribas, ya ayyana shi a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo bisa zargin ɗakko hayar yan daba da ake zargin ƴan asiri ne su tarwatsa taron tantancewa.

Ku saurari ƙarin bayani….

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here