PDP Zuwa APC: Kotu ta Dage Zaman Shari’a Kan Sauya Shekar Gwamnan Jahar Cross River

 

Babban kotun tarayya dake Abuja ta dage zaman shari’a kan karar da jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta shigar na kwace kujerar Gwamnan jihar Cross River, Farfesa Ben Ayade da mataimakinsa, Ivara Esu.

Jam’iyyar hamayyar ta shigar da karar ne saboda sauya shekarsu zuwa jam’iyyar All Progressive Congress (APC).

An shirya zama yanke hukunci kan lamarin yau amma Alkali Taiwo Taiwo ya dage zaman zuwa ranar 6 ga Afrilu, 2022, rahoton ChannelsTV.

Abinda ya fadawa yan majalisa ka iya fadawa kansa

Babbar kotun tarayya da ke zama a Abuja, ta sallami wasu mambobin majalisar dokokin jihar Cross River su 20 a ranar Litinin, 21 ga watan Maris.

Kotu ta kwace kujerun su ne saboda sauya sheka daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) zuwa jam’iyyar All Progressive Congress (APC) mai mulki.

Kotun, a wani hukunci da mai shari’a Taiwo Taiwo ya yanke, ya riki cewa ya zama dole yan majalisar su sauka daga kujerunsu kasancewar sun yi watsi da jam’iyyar da ta dauki nauyin kawo su kan mulki.

Hukuncin ya biyo bayan wata kara mai lamba FHC/ABJ/CS/975/2021, da PDP ta shigar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here