Babbar Kotun a Lagos ta Soke Shari’ar Gwamnatin Najeriya Kan ƙwato Naira Tiriliyan 70

 

Babbar kotun tarayya a Lagos ta soke wata shari’a da gwamnatin tarayyar Najeriya ke neman ƙwato wasu kuɗi naira tiriliyan 70 da take zargin na ajiye a asusun bankuna 29 na wasu da take zargin sun sace su.

Mai shari’a Peter Lifu ya zartar da cewa lauyoyin gwamnatin da kuma wasu masu zaman kansu da ta ɗauka haya ba su mayar da hankali sosai a kan shari’ar ba saboda haka ya soke shari’ar.

Alƙalin ya yi matuƙar mamakin yadda lauyan gwamnatin tarayya a shari’ar Mohammed Ndarani, (SAN) daga baya kuma Femi Falana (SAN) kwatsam suka nuna alamun ja da baya a kan shari’ar ta zargin sace kuɗin wadda ke da muhimmanci matuƙa ga al’umma.

Gwamnatin tarayyara Najeriya da ministan shari’a su ne masu zargi waɗanda ake zargin ko kuma masu kare kansu 19 yawanci bankuna ne da kamafanin mai na ƙasar NNPC da kuma kamafanin mai na Agip.

Bankuna su ne Zenith Bank Plc, Polaris Bank Plc, Citi Bank Ltd, Stanbic IBTC Bank Plc, Standard Chartered Bank Plc, Sterling Bank Plc.

Sauran su ne Union Bank Plc, Unity Bank Plc, Keystone Bank Plc, Heritage Bank Plc, First Bank Plc, United Bank For Africa Plc, Fidelity Bank Plc, Eco Bank Plc, Guaranty Trust Bank Plc, Wema Bank Plc, Access Bank Plc.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here