Almundahana: Kotu ta Wanke Saminu Turaki

 

Wata babbar kotun tarayya da ke zama a garin Dutse ta wanke tsohon gwamnan jihar Jigawa Saminu Turaki daga tuhumar da hukumar EFCC ke yi masa ta almundahana da kuɗi naira biliyan 8.3.

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya ce ta kai tsohon gwamnan, da wasu kamfanoni uku, ƙara tun a shekara ta 2007 kan laifuka 33.

Alƙalin da ya yanke hukunci, mai shari’a Hassan Dikko, ya yi watsi da dukkanin tuhume-tuhume da ake wa tsohon gwamnan bisa hujjar rashin mayar da hankali daga ɓangaren waɗanda suka shigar da ƙara.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here