Kungiyar Dillacin Man Fetur ta Arewacin Najeriya ta Tafi Yajin Aiki

 

A yau ne Kungiyar masu dillacin man fetur na arewacin Najeriya suka fara yajin aiki, bayan da suka zargi hukumomin da ke kula da safarar man fetur ta ruwa da na tudu da rike musu kudin dako tsawo watanni 8.

Wannan dalili ne yasa suka fara yajin aikin gargadi na tsawon kwana uku, tare da dakatar da kai mai zuwa duk wani gidan mai dake jihohin arewacin kasar.

Wakilinmu da ke Kano da ya ziyarci NNPC defo da ke unguwar Hotoro ya ruwaito cewa ya ga wasu motocin makare da mai, amma an hana su tafiya sakamakon yajin aikin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here