Ya Kamata Limamai da Fastoci su Daina Cusa wa Mabiya ƙiyayya – Alhaji Sa’ad Abubakar III

 

Sarkin Musulmin Najeriya, Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya ce wasu ƴan barandan siyasa na barazana ga tarihin Najeriya da na al’ummarta.

A cikin wani saƙon taya murna na bukin Easter da Sarkin Musulmin ya aika wa shugaban Ƙungiyar Kiristocin Najeriya, Daniel Okoh, ya ce lamarin ‘aiki ne na Shaiɗan, wanda makircinsa mai rauni ne.’ Kamar yadda Alƙur’ani ya bayyana.

A cikin jawabin nasa, wanda ya samu sa hannun Mataimakin shugaban Majalisar Ƙoli ta Lura da Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya, Farfesa Salisu Shehu, Sarkin ya buƙaci shugaban na CAN ya haɗa hannu da Ƙungiyar ta Musulunci wajen ganin an rage yadda limamai da fasto-fasto ke cusa wa mabiyansu ƙiyayya ta siyasa da kuma munanan kalamai.

Daga ƙarshe mai alfarma Sarkin Musulmin ya taya al’ummar Kirista murnar zagayowar ranar Easter tare da addu’ar ci gaban Najeriya

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here