Rundunar Ƴan Sandan Jihar Zamfara sun Tarwatsa Ƴan Fashin Daji

 

Rundunar ƴan sanda a jihar Zamfara ta ce jami’anta sun tarwatsa wani yunƙurin ƴan bindiga na kai hari a wani ƙauye da ke yankin ƙaramar hukumar Tsafe.

Haka nan jami’an sun samu nasarar hallaka ƴan bindigan guda biyu.

A cikin wata sanarwa da ta samu sa hannun mai magana da yawun rundunar a jihar, Mohammed Shehu, ta ce lamarin ya faru ne ranar Lahadi, inda aka yi artabu tsakanin jami’an ƴan sandan da kuma maharan.

Sanarwar ta ce baya ga waɗanda aka kashe, wasu maharan sun tsira da munanan raunuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here