LP ta Musanta Tattaunawa da PDP da NNPP Domin Samar da Jam’iyya Guda

Jam’iyyar Labour mai hammaya a Najeriya ta musanta batun tattaunawa da takwarorinta na PDP da NNPP domin samar da jam’iyya guda da za ta tunkari jam’iyya mai mulki ta APC a zaɓe mai zuwa.

Jam’iyyar ta Labour ta bayyana haka ne bayan da wasu daga cikin jaridun Najeriya suka rawaito cewar ana wata ganawa tsakanin ‘yan takarar shugabancin ƙasar na PDP Atiku Abubakar, da na NNPP Rabi’u Kwankwaso, da Peter Obi don haɗewa waje guda.

Mai magana da yawun jam’iyyar Labour na ƙasa, Dr Tanko Yunusa ya ce iya abun da suka sani shi ne, akwai tattaunawa ta fahimta da ake yi tsakanin dan takararsu da na NNPP da na PDP, wanda kuma ba shi da alaka da batun samar da jam’iyya ko wani abu makamancin hakan.

Haka kuma Dr. Tanko Yunusa ya ce ko da za a haɗe ɗin ma to sai dai a ba su jan ragamar ta fi da komai, kuma a sa su a gaba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com