Gwamnoni da Suka Gaza cin Zaben Sanata: Mai Zabe Shine Sarki – Buhari

Biyo bayan sakamakon manyan zabukan 2023, Shugaba Buhari ya tabbatar da cewa lallai mai zabe shine sarki.

Shugaban na Najeriya ya ambaci yadda wasu gwamnoni suka gaza cin zaben sanata, yana cewa hakan na nufin a yanzu babu wata tabbataciyar hanyar samun mulki.

Idan za a iya tunawa irinsu Gwamna Okezie Ikpeazu na Abia, Samuel Ortom na jihar Benue sun sha kaye a zaben neman zuwa majalisar dattawa.

FCT, Abuja – Shugaba Muhammadu Buhari, a ranar Alhamis 6 ga watan Afrilu, ya ce kada wani ya sake raina karfin ikon da masu zabe ke da shi a Najeriya.

Shugaban, yayin da ya ke duba zuwa ga sakamakon zabukan 2023, ya tabbatar cewa zamanin samun mulki cikin sauki ya kau.

Shugaban na Najeriya ya ce zabukan na 2023 sun nuna wayewa na masu kada kuri’a a Najeriya idan aka zo batun zaben shugabanni, ya kuma ce dimokradiyya a kasar na kara karfi.

Buhari ya bayyana abin da ke zuciyarsa yayin da ya karbi bakuncin sabon sarkin Dutse, babban birnin jihar Jigawa, Alhaji Muhammad Hamin Nuhu Sunusi, a gidan gwamnati a Abuja.

Ya kara da cewa ya yi mamakin yadda wasu gwamnoni da ke kan mulki suka gaza cin zaben sanata. A cewarsa, hakan na nufin mai kada kuri’a, tabbas shine sarki idan ana maganar zabe.

A cikin wata sanarwa da Garba Shehu, hadimin shugaban kasa na musamman kan watsa labarai ya fitar, shugaban kasar ya ce

“Wannan shaida ne da ke nuna dimokradiyyarmu ta girma kuma masu jefa kuri’a sun waye. Abin da ya bani mamaki shine talaka wanda galibi ana raina shi ya nuna cewa ya fahimci siyasa.A koyaushe ana zaton idan kayi shekara takwas a gwamna za ka tafi majalisa ka karasa aikin ka. Babu wanda ya isa ya raina masu jefa kuri’a a Najeriya yanzu. Siyasa za ta kara wahala, daga yanzu.”

Gwamnoni da suka gaza cimma burinsu na zuwa majalisa

Idan za a iya tunawa, gwamnoni masu ci – Okezie Ikpeazu na Abia, Samuel Ortom na Benue, Ifeanyi Ugwuanyi na Enugu, Simon Lalong na Plateau, Darius Ishaku na Taraba, Ben Ayade na Cross Rivers da Abubakar Bagudu na Kebbi duk sun sha kaye a zaben neman zuwa majalisar dattawa.

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, na APC shima ya gaza samun damar zarcewa kan kujerarsa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here