Mazauna unguwar Gama daka Kano sun koka kan ayyukan da Gwamnan Kano ya fara kuma bai kammala ba yayin zaben cike gurbi a mazabar da akai a yayin zaben 2019 da ya gabata.

Auwal Danlarabawa daya daga cikin mazauna unguwar Gama ya bayyana kokensu kamar haka:

“Burtsatsen Masallacin Yara layin Makarantar adfalu tunda aka haka aka barta ba tare da an saka solar ba Ballantana Batir zuwa karasa ta yadda Za’a anfana da ita kuma mun san yadda akayi kokarin wannan aikin Dan a Tallafawa Al’umma musanman akan Matsalar ruwan Sha da ake fama dashi a Mazabar Gama.

Dama wasu kuma muna Kara Kira da a duba solar din da aka Sakawa Burtsatsen Dan akwai bukatar ya zama kowacce tana da Batir kamar yadda ka umarci Ayi ingantaccen aiki wanda Za’a Dade ana anfani da tagomashin da ka kawo wannan Mazaba.

Muna Fatan Za’a duba wannnan koke tare da share mana Hawaye Dan kar a cigaba da cewa Rijiya ta bayar guga Ya Hana.”

The post Mutanan Gama sun koka kan ayyukan da aka fara lokacin zabe ba’a gama ba appeared first on Daily Nigerian Hausa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here