Hukumar da ke Sanya Ido a Kan Kafafen Watsa Labarai ta Kwace Lasisin AIT,Silverbird da FM

 

Hukumar da ke sanya ido a kan kafafen watsa labaran Najeriya, National Broadcasting Commission (NBC) ta kwace lasisin wasu kafafen watsa labarai saboda gaza sabunta shi.

A wata sanarwa da shugaban hukumar, Malam Balarabe Shehu Illela, ya fitar ranar Juma’a ya ce kafafen watsa labaran da aka kwace lasisinsu sun hada da Silverbird TV, AIT, Raypower FM, Rhythm FM da karin wasu da dama bisa gaza biyan kudin da suka kai N2.66 bn don sabunta lasisin nasu.

Sanarwar ta ce an dauki matakin ne bayan an wallafa jerin kafafen watsa labarai da ba su sabunta lasisinsu ba.

A cewar hukumar, an bai wa kafofin watsa labaran karin makonnin biyu a watan Mayu domin su sabunta lasisinsu ko kuma su fuskanci yiwuwar saoke su amma suka ki.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here