ENDSARS: An ci Tarar Gidajen Talabijin na Channels, AIT, Arise

 

  Muƙaddashin daraktan hukumar Farfesa Armstrong Idachaba, shi ne ya bayar da sanarwar tarar a yau Litinin a Abuja, inda ya ce za su biya tarar naira miliyan uku kowannensu.

  An yaɗa hotuna da bidiyo na boge a tsakanin mako biyu da aka shafe ana zanga-zangar nuna ɓacin rai game da ayyukan rundunar ‘yan sanda a Najeriya, wadda aka yi wa laƙabi da EndSars – wato a rushe rundunar SARS mai yaƙi da fashi da makami.

BBC ta bincika tare da bankaɗo gaskiya da ƙaryar wasu daga cikinsu a wannan labarin.

  An ci tarar gidajen talabijin ɗin uku ne saboda “yaɗa hotunan da ba a tantance ba na harbe-harben da ake zargin an yi”.

  Tun a baya, NBC ta gargaɗi kafofin yaɗa labarai da su yi taka-tsantsan wurin yaɗa hotunan da suka samu daga shafukan sada zumunta, tana mai cewa rashin tantance sahihancinsu ka iya jawo hatsaniya a ƙasa baki ɗaya

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here