Mutane 2 Sun Rasa Rayukansu a Zaben Deleget na PDP a Jahar Osun

Akalla mutum biyu sun rasa rayukansu yayinda da dama suka jikkata a zaben deleget na jam’iyyar People’s Democratic Party PDP dake gudana a jihar Osun.

Kakakin hukumar yan sandan jihar, Yemisi Opalola, ta tabbatar da hakan ga manema labarai ranar Laraba a Osogbo, TVCNews ta ra

waito. A cewarta, an kashe wani matashi mai suna Toheeb Mutallib a Oke Oba, Agberire a karamar hukumar Iwo, yayinda aka kashe wani dan jam’iyyar siyasa Aremu Olamide a Ipetumodu, karamar hukumar Ife-North.

asu masu idanuwan shaida sun bayyana cewa an yiwa mutane da dama jina-jina yayinda yan daba suka kai hari garuruwa irinsu Ede, Osogbo, Odo-Otin, Olorunda, Iwo, da sauransu.

Hakazalika an bankawa mota wuta a Ipetumodu sakamakon rikici tsakanin yan daba.

Kawo yanzu Alkalin zaben, Gwamnan jihar Adamawa, Ahmad Fintiri, basu isa wajen tattara zabe ba.

Za’a zabi mutum uku-uku a gundumomin jihar 332 kuma su zasu kada kuri’a a zaben fidda gwanin dan takaran gwamna a ranar 7 ga Maris, 2022.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here