Sababbin Tuhume-Tuhume da Gwamnatin Najeriya ta Gabatar Kan Nnamdi Kanu

 

Gwamnatin Najeriya ta shigar da sababbin kararraki 7 kan jagoran ‘yan awaren IPOB, Nnamdi Kanu a gaban babban kotun tarayya da ke Abuja.

Kararrakin sun kunshi cin amanar kasa da ta’addanci wadanda suka kasance kari kan tuhume-tuhume da ake masa tun 2016.

Kotu ta sanar da Alhamis 21 ga watan Oktoba a matsayin ranar sauraron kararrakin.

Wannan na zuwa ne yayin da ƙungiyar Ohanaeze ta ƙabilar Ibo ta yi kira ga gwamnatin Najeriya ta tabbatar an kai Kanu kotu.

Jaridar Vanguard a Najeriya ta rawaito cewa ƙungiyar ta Ohanaeze ta ce bayyanar Kanu a kotu na da muhimmanci don nuna wa duniya cewa Nnamdi Kanu na ciki ƙoshin lafiya kuma za a yi masa adalci a lokacin shari’a.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here