Taliban na ba da Haɗin Kai ga Amurka Dangane da Kwashe Amurkawa a Afghanistan – Joe Biden

 

Joe Biden na Amurka ya bayyana cewa, Amurka ba ta fuskantar kalubalen kwashe mutanenta a Afghanistan.

A cewarsa, matsalar ita ce debe mutanen da suke goya wa Amurka baya a kasar wadanda ba sa son zama da Taliban.

Shugaban ya ce Amurka za ta ci gaba da zama a kasar har sai ta kwashe dukkan Amurkawa a kasar.

Afghanistan – Shugaba Joe Biden na kasar Amurka ya ce Taliban na ba da hadin kai ga Amurka dangane da kwashe Amurkawa a Afghanistan, Daily Trust ta tattaro.

Tun bayan rugujewar gwamnati a Afganistan a makon da ya gabata, sojojin Amurka suna kwashe ‘yan Amurka daga kasar.

A cikin hirar sa ta farko tun bayan da Taliban ta karbe iko a Afghanistan, Biden ya fadawa ABC News cewa duk da hadin kan da ake bayarwa wajen fitar da Amurkawa daga kasar, “muna kara samun matsala” wajen kwashe ‘yan Afghanistan da ke hada kai da Amurka.

Ya ce:

“Suna ba da hadin kai, suna barin ‘yan Amurka su fita, ma’aikatan Amurka su fita, ofisoshin jakadanci su fita, da dai sauransu, amma muna samun karin wahalar samun wadanda suka taimaka mana lokacin da muke can.”

Ya kuma ce sojoji ba za su bar wani Ba’amurke a Afghanistan ba, koda kuwa hakan na nufin zama cikin Kabul na tsawon shekaru fiye da yadda aka amince.

Biden ya kara da cewa:

“Idan akwai sauran jama’ar Amurka da suka rage, za mu zauna har sai mun fita da su duka.”

Jaridar New York Times ta ce, da aka tambaye shi ko yana tunanin magance rikicin zai iya tafiya?

Biden ya ce:

“A’a. Za mu koma hangen nesa mu duba, amma ra’ayin cewa ko ta yaya, akwai wata hanyar da za mu fita ba tare da hargitsi ba, ban san yadda hakan ke faruwa ba.”

‘Yan majalisar dokokin Amurka sun matsa a kara wa’adin kwashe Amurkawa a Afghanistan

‘Yan majalisar dokokin Amurka sun matsa wa Biden ya tsawaita wa’adin kwashewar zuwa ranar 31 ga watan Agusta da ya tsara don ficewa gaba daya.

Amurka ta ce ta kwashe kusan mutane 6,000 daga Afghanistan tun ranar Asabar amma dubunnan Amurkawa da dubun dubatan ‘yan Afghanistan da ke son barin kasar na ci gaba da kasancewa kuma tana da jinkirin debewar lamarin da ke jefa rayuwa cikin hadari.

‘Yan mata masu ilimi, tsoffin masu fassara ga sojojin Amurka da sauran ‘yan Afghanistan da ke cikin hadarin gaske daga Taliban sun yi kira ga gwamnatin Biden da ta gaggauta gwaso su zuwa Amurka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here