WTO ta ƙaddamar da Cibiyar Tabbatar da Ingancin Abinci a Najeriya

 

Ƙungiyar cinikayya ta duniya WTO ta ƙaddamar da wata cibiyar haɓaka kasuwanci a Najeriya domin tabbatar da ingancin abinci.

Cibiyar wani shiri ne na duniya da ke neman haɓaka hanyoyin inganta abinci da dabbobi da lafiyar tsirrai a ƙasashe masu tasowa ta hanyar ƙarfafa gwiwar amfani da tsare-tsare managarta.

Da take magana a taron ranar Talata, daraktar gudanarwar WTO, Dakta Ngozi Okonjo-Iweala ta yi bayani cewa duk da Najeriya tana da ƙwarewa wajen samarwa da kuma fitar da wake da riɗi, rashin amincewa da abubuwan biyu na ci gaba da zama babban ƙalubale saboda rashin kyawun sufuri da alkinta albarkatun gona zuwa sauran sassan duniya.

Najeriya ce ƙasa ta uku da ta fi samar da riɗi a Afirka inda ta samar da metric tan 500 a 2022 da fiye da metric tan fiye da miliyan 5.2 na busasshen wake da ake samarwa duk shekara.

A cewar Iweala, cibiyar za ta ƙarfafa gwiwar manoman Najeriya wajen samar da albarkatun gona da za su yi daidai da yadda ake samar da su a ƙasashen duniya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here