EndSars: Ƴan Sandan Lagos sun Buɗe Wuta ga Dubban Jama’a masu zanga-zanga a Jahar Ta su.

Ƴan sandan kwantar da tarzoma sun buɗe wa dubban masu zanga-zangar EndSars wuta a dandalin Lekki toll gate da ke birnin Legas a kudancin Najeriya da yammacin Talata.

Masu zanga-zangar sun ci gaba da yin ta ne bayan da gwamnatin jihar ta sanya dokar hana fita ta sa’a 24 a jihar a ranar Talata da safe sakamakon ƙona wani ofishin yan sanda da aka yi.

BBC tana cikin nuna bidiyon ci gaban zanga-zangar kai tsaye a shafinta na Facebook a lokacin da aka fara harbe-harbe da bindiga a wajen.

Dubban mutane ne suka sake taruwa a dandalin na Lekki toll gate suna ci gaba da zanga-zangar.

Amma nan da nan sai komai ya hargitse wajen ya cuɗe. Babu tabbas kan ko mutum nawa ne suka jikkata a lamarin wanda ya faru da misalin ƙarfe 6.45 na yamma agogon Najeriya.

Tuni dai zanga-zangar ta rikiɗe zuwa rikici tsakanin masu yin ta da wasu da ake zargin ƴan daba ne a wasu manyan biranen ƙasar da suka haɗa da babban birnin tarayya Abuja.

Wakilin sashen BBC Pidgin ya ce ya ga mutum ɗaya da ya jikkata.

Tuni a wasu jihohin ma aka sanya dokar hana fita ta sa’a 24 kamar Jos da Ekiti da Abia.

Dama tun da farko a ranar Talatar Babban Sifeton ‘yan sandan Najeriya ya umarci baza ‘ƴan sandan kwantar da tarzoma a duk faɗin ƙasar.

Sanarwar Muhammad Adamu, na zuwa ne yayin da ake samun ƙaruwar tashin hankali a wasu jihohi sakamakon zanga-zangar nuna adawa da cin zalin da ake zargin jami’an ‘yan sanda na yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here