‘Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da DPO a Jihar Nasarawa

Rahotanni daga jihar Nasarawa da ke tsakiyar Najeriya na cewa an yi garkuwa da shugaban jami’an yan sanda na karamar hukumar Nasarawa-Eggon.

Rahotannin sun ce CSP Haruna AbdulMalik na sintiri ne a ranar Laraba da daddare tsakanin Eggon-Akwanga, a lokacin da yan bindiga suka fara harbi ba-ji-ba-gani, kafin su yi awon gaba da shi.

Wata majiya ta ce DPO ya samu labarin cewa ‘yan bindiga na hari a karamar hukumar Nasarawa Eggon, kuma yayin da yake kokarin kai dauki ne yan bindigar suka sace shi.

Al’ummar yankin sun bayyana CSP Haruna AbdulMalik a matsayin jajirtaccen dan sanda, da ke taka rawa wurin tabbatar da tsaro a Nasarawa-Eggon.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here