Ƴan Bindiga Sun Hallaka Mutane Biyu a Katsina

 

Rundunar ƴan sanda a jihar Katsina da ke arewacin Najeriya ta tabbatar da cewa ƴan fashi sun kashe mutum biyu lokacin da suka kai hari a wani ƙauye da ke ƙaramar hukumar Ƙanƙara.

Sai dai rundunar ta ce jami’anta sun samu nasarar koran ƴanfashin tare da ƙwato mutum 18 waɗanda aka yi yunkurin sacewa.

Mai magana da yawun rundunar ƴansanda a jihar ta Katsina, SP Gambo Isa ya ce mutane biyun da suka mutu an hallaka su ne kafin ƴansandan su kai ɗauki.

Maharan a kan babura sun kai farmaki ne a kauyen na Gidan Baushe da tsakiyar daren Laraba.

Sai dai bayan da aka sanar da ƴansanda game da harin, sun kai ɗauki cikin hanzari inda suka kori maharan tare da ƙwato wasu daga cikin mutanen da suka sace.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here